in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan, Chad, da Faransa suna aiki tare don ceto dan kasar Faransan da aka yi garkuwa da shi
2017-03-27 09:36:19 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Sudan ta sanar a jiya Lahadi cewa, kwararrun masu bincike na kasashen Sudan, da Faransa da kuma Chadi suna yin aiki tare domin gano wani dan kasar Faransar da aka yi garkuwa da shi a Chadi kuma aka kaura da shi zuwa kasar Sudan.

Ministan harkokin wajen Sudan Ibrahim Ghandour, ya shedawa 'yan jaridu cewa, tuni aka riga aka sanar da ma'aikatar harkokin waje da hukumar binciken sirri da hukumomin tsaro da sojoji game da yin garkuwa da wannan bafaranshe.

Ya kara da cewa, kasar Sudan tana cigaba da tuntubar hukumomin kasar Faransa da abin ya shafa, kamar hukumar tsaron kasar Faransar, da kuma gwamnatin kasar Chadi ta hanyar tuntubar jakadun kasashen domin gano mutumin da aka yi garkuwa da shi.

Babban jami'in tsaron kasar Chadi Ahmed Mohammed Bashir, ya fada tun da farko cewa, an kame wannan bafaranshe ne a wani kamfanin hakar ma'adanai inda aka yi garkuwa da shi zuwa wani waje dake da tazarar kilomita 200 a kudancin birnin Abeche dake kasar Chadin a ranar Alhamis data gabata kafin daga bisani aka tusa keyarsa zuwa kasar Sudan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China