in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan tace shiga tsakanin da kasahen duniya keyi wajen tattaunawa zai kawo zaman lafiya
2017-04-02 13:30:26 cri
A jiya Asabar gwamnatin Sudan ta sanar da cewa tattaunawar shiga tsakani da kasashen Jamus, Uganda da sauran kasashen duniya ke jagoranta, za ta taimaka wajen rarrashin 'yan tawayen da su amince da cimma matsaya da gwamnatin Sudan.

Cibiyar yada labarai ta kasar SMC, ta rawaito Ministan yada labaran kasar Sudan Ahmed Bilal Osman, yana cewa, ana fata kungiyoyin 'yan tawayen da bangaren gwamnatin kasar zasu zauna a teburin sulhu domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar kasar.

Bilal ya jaddada aniyar gwamnatin Sudan wajen amincewa da shiga yarjejeniyar da bangarorin 'yan tawayen na (SPLM)/arewaci da kuma na yankin Darfur bisa ka'idojin da yarjejeniyar ta tanada.

Dama dai tun a watan Maris na shekarar 2016 ne, gwamnatin Sudan ta sanya hannu kan wata yarjejeniyar a birnin Addis Ababa na kasar Habasha a matsayin share fage da kungiyar tarayyar Afrika AU ta gabatar, wanda ake fatar zai tabbatar da shirin tsagaita bude wuta a kudancin Kordofan, da tekun Nile da yankin Darfur, wanda zai bada damar shiga shirin tattaunawar zaman lafiyar tsakanin gwamnatin Sudan da 'yan tawayen kasar domin samun dawwamammen zaman lafiya wanda aka tsara tattaunawar a halin yanzu a Khartoum.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China