in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masana tsaro na Afrika sun bukaci a dauki matakan yaki da yan ta'adda na kasashen waje
2017-04-06 09:54:55 cri
A jiya Laraba ne kasashen Afrika suka bukaci a dauki kwararan matakai don tunkarar kungiyoyi masu dauke da makamai a nahiyar domin dakile ayyukansu da kuma 'yan ta'adda daga wasu kasashen duniya.

Kwamitin kwararru masanan tsaro na Afrika wato CISSA, ya kuma bukaci a dinga musayar bayanai game da duk wata kungiya mai zaman kanta dake da mummunar manufa a fadin nahiyar.

Wakilai daga kasashe mambobin CISSA, da na kasa da kasa da shiyya shiyya, sun kammala wani taron karawa juna sani na shiyya shiyya na tsawon kwanki 3 a birnin Khartoum na kasar Sudan, domin tattaunawa game da batun tsaro da zaman lafiyar Afrika.

Mataimaki na farko ga shugaban kasa, kana firayiministan kasar Sudan Bakri Hassan Saleh, ya bayyana wannan taron a matsayin wani babbban buri na nahiyar Afrika, ya kara da cewa masu adawa da ci gaban bil Adama za'a iya yin galaba a kansu, ko na cikin gida ne ko kuma na kasashen waje ko kuma kungiyoyi masu zaman kansu masu mugaye manufofi.

A wani labarin kuma, babban sakataren CISSA, Shimelis Woldesemayat, ya ce za'a mai da hankali sosai kan barazanar masu shirya ta'addanci, da masu dauke da makamai da kungiyoyi masu mugayen manufofi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China