in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana goyon bayan bincike na gaskiya game da amfani da sinadarai masu guba a Syria
2017-04-06 09:14:08 cri
Jakadan kasar Sin ya ce kasarsa tana goyon bayan hukumar haramta amfani da sinadarai masu guba OPCW da sashen MDD, game da gudanar da cikakken bincike da nufin binciko amfani da sinadarai masu guba a Syria.

Liu Jieyi, wanda shi ne zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, ya yi wannan kira ne a lokacin taron kwamitin tsaro na MDD wanda ya gudanar game da nazartar zargin da ake yi na yin amfani da sinadarai masu guba a kasar Syria.

An bada rahoton mutuwar mutane 70, kana wasu 200 kuma sun samu raunuka a wani harin da aka kai ta hanyar amfani da iskar gas kan 'yan tawaye a yankin Idlib dake arewa maso yammacin Syria.

Kasar Sin ta yi Allah wadai da yin amfani da sanadarai masu guba a kowace kasa ta duniya, ko kuma daga kowace irin kungiya ko kuma wani mutum a kowane irin yanayi, Mista Liu ya ce muna yin Allah wadai da kakkausar murya game da kaddamar da hari kan fararen hula.

Ya kara da cewa ya zama wajibi a binciko wadanda ke da alhakin aikata irin wadannan laifuka na yin amfani da sinadarai masu guba don hukunta su.

Liu ya jaddada muhimmancin daukar matakai na siyasa a matsayin sahihiyar hanya ta warware rikicin Syria. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China