in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a dauki matakai mafiya dacewa, don tinkarar batun Darfur
2017-04-05 13:50:29 cri
Zaunannen wakilin Sin dake MDD Liu Jieyi, ya bayyana a jiya Talata cewa, batun Darfur na kasar Sudan na da alaka da fannonin siyasa, da tsaro, da ci gaban kasa, da ma ayyukan jin kai da sauransu, don haka ya kamata a dauki matakai mafiya dacewa, ta yadda za a kai ga warware batun ta hanyar siyasa.

Liu Jieyi wanda ke jawabi yayin taron kwamitin sulhun MDD, ya ce kamata ya yi kasashen duniya su ci gaba da nuna goyon baya, ga aikin shiga-tsakani da rukunin gudanarwar kungiyar AU ke gudanarwa, da gaggauta taimakawa gwamnatin kasar Sudan, wajen cimma yarjejeniya a tsakaninta da tawagar dakaru da masu adawa.

Sauran matakan sun hada da warware matsaloli ta hanyar gudanar da shawarwari, da neman warware batun yankin Darfur cikin lumana. Kana yana fatan bangarori masu bada gudummawa, za su cika alkawarinsu na samar da gudummawa, da taimakawa gwamnatin kasar Sudan, wajen gina ababen more rayuwa, da inganta karfin samun bunkasuwa a yankin Darfur, don samar da ci gaban tattalin arziki, da zamantakewar al'umma mai dorewa a yankin. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China