in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara kada kuri'un jin ra'ayin jama'a a yankin Darfur na Sudan
2016-04-11 20:23:29 cri
A ranar 11 ga wata, aka fara kada kuri'un jin ra'ayoyin jama'a na kwanaki uku a yankin Darfur na kasar Sudan, ana son tsaida kuduri ne dangane da ko za a hade wasu jihohi 5 su zama babbar jiha guda a wannan yanki ko a'a.

Bisa shirin kada kuri'un da gwamnatin kasar Sudan ta tsara, idan jama'ar yankin Darfur sun nuna goyon baya a hade jihohi 5, za a kafa kwamitin tsarin mulki mai 'yancin kai a wannan yankin, domin gudanar da harkokin hukumomin gwamnati a yankin Darfur. Idan kuma jama'ar sun ki amincewa, za a kiyaye jihohin biyar, sannan a wargaza hukumar wucin gadi wacce keda iko a wannan yanki. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China