in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sace ma'aikatan MDD 3 a Darfur
2016-11-29 11:11:10 cri
An sace wasu ma'aikata 3 na ofishin Sudan na hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD ta UNHCR, a garin Geneina, hedkwatar jihar West Darfur ta kasar Sudan, a ranar Lahadi. Har yanzu ba a san dakarun da suka sace wadannan mutane ba.

Wani mai magana da yawun jihar West Darfur ya yi bayani kan abun da ya faru ga wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua ta wayar tarho, inda ya ce al'amarin sace mutanen ya abku ne a yammacin ranar Lahadi bisa agogon wurin. A cewarsa, wasu dakaru sun kutsa kai cikin ofishin hukumar UNHCR dake garin Geneina, tare da yin awon gaba da ma'aikatan ofishin 3, sa'an nan suka bar wurin cikin motoci.

An ce yanzu haka jami'an tsaron jihar West Darfur suna kokarin bincike kan dakarun da suke da alhakin aikata wannan danyen aiki, kuma a shirye suke don kubutar da mutanen da aka sace, duk lokacin da aka tabbatar da wurin da ake tsare da su. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China