in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da shirin horar da manema labaru a cibiyar musayar ra'ayi tsakanin Sin da Afirka a fannin watsa labaru
2017-03-01 19:39:56 cri

A yau Laraba ne aka kaddamar da shirin horar da manema labaru karo na 4, a cibiyar musayar ra'ayi tsakanin Sin da Afirka ta fuskar watsa labaru dake birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Shugaban majalissar harkokin diplomasiyyar al'umma ta kasar Sin mista Li Zhaoxing, ya halarci bikin kaddamar da taron, inda ya kuma gabatar da jawabi.

Cikin jawabin na sa, Mr. Li yayi fatan cewa, manema labaru na kasashen Afirka wadanda suka halarci shirin, za su kara fahimtar manufar kasar Sin, da samar da gudunmawa ga hadin gwiwar Sin da Afirka ta fuskar watsa labaru.

Kaza lika a wajen taron, ma'aikaciyar jaridar "The Leadership" ta tarayyar Najeriya Bukola Ogunsina, ta gabatar da jawabi a madadin sauran manema labaru na kasashen Afirka, inda ta ce za su yi amfani da wannan dama, domin nazari kan ilimin da ya shafi kasar Sin, da harkar watsa labaru, ta yadda za su kasance masu taimakawa musayar ra'ayi tsakanin Sin da nahiyar Afirka. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China