Rahotanni daga kasar Mali na cewa wani Bam da aka dana jikin wata mota ya hallaka mutane a kalla 80, baya ga wadanda suka jikkata a wani wuri dake kusa da sansanin sojojin kasar dake Gao.
Wata majiyar asibitin yankin ta bayyana cewa, motar dake dauke da Bam din ta tarwatse, tare da hallaka mutanen dake daura da ita, da sanyin safiyar Larabar nan a garin na Gao dake arewacin kasar ta Mali.(Saminu Alhassan)