in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta shiga sahun kasashe masu fitar da Siminti
2017-03-21 19:59:31 cri
Ministan ma'aikatar raya albarkatun kasa a tarayyar Najeriya Kayode Fayemi, ya ce yanzu haka Najeriya ta wadatu da yawan siminti da ake sarrafawa a cikin kasar, har ta kai ana fitar da shi zuwa kasashen ketare.

Mr. Fayemi wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, ya ce hakan na da nasaba da kwazon da kamfanin siminti na Dangote ya nuna a fannin zuba jari, karkashin tsare tsaren da gwamnatin tarayyar kasar ke marawa baya. Ya ce abun alfahari ne ganin cewa a baya Najeriyar na shigo da kaso kusan 60 bisa 100 na simintin da ake bukata a cikin kasar daga ketare, amma yanzu ta kai ana fitar da shi zuwa kasashen waje.

Ministan wanda ya jagoranci wata tawagar gwamnati zuwa kamfanin Simintin na Dangote dake Ibese a jihar Ogun dake kudancin Najeriya, ya ce gwamnatin kasar mai ci, na farin ciki da rawar da kamfanin ke takawa wajen bunkasa sana'ar samar da Siminti a kasar.

A watan Fabarairun da ya shude ne, babban manajan daraktan kamfanin Onne Van der Weijde, ya bayyana cewa, bisa alkaluman kididdigar hajoji da ribar da kamfanin ya samu a shekarar 2016, kamfanin na fitar da kusan tan dubu dari hudu na Simintinsa zuwa kasashe makwaftan Najeriya. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China