in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Minista: Najeriya za ta fara fitar da 'ya'yan kanju da aka sarrafa zuwa ketare nan da 2019
2017-03-15 09:51:15 cri
Gwamnatin Najeriya ta kuduri aniyar samu riba mai yawa ta hanyar cinikin kwallon kanju da aka sarrafa a kasuwannin kasashen duniya a matsayin wani bangare na aniyar gwamnatin kasar na farfado da aikin gona don gina ci gaban kasar.

Ministan noma da raya karkara na kasar Audu Ogbeh shi ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Legas, ya ce Najeriyar za ta fara fitar da 'ya'yan kanju da aka sarrafa zuwa kasashen ketare nan da shekarar 2019, ya ce a halin yanzu ton guda na 'ya'yan kanju da aka sarrafa ya kai dala dubu 10 a kasuwannin duniya.

Ya kara da cewa ya fi dacewa a fitar da 'ya'yan kanju da aka sarrafa zuwa kasashen ketare a maimakon wanda ba'a sarrafa shi ba.

Ogbeh ya ce gwamnatin kasar tana bin matakan da suka dace domin ganin 'ya'yan kanju sun samu karbuwa a kasuwannin duniya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China