in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 9 sun mutu a wani hari da ake zargin Boko Haram a yankin arewa mai nisa na Kamaru
2017-03-19 12:14:15 cri

Wasu mahara 7 da sojojin Kamaru 2 sun mutu, a wani hari da ake zargin mayakan Boko Haram da kaddamarwa a yankin arewa mai nisa na Jamhuriyar Kamaru.

Wata majiya daga rundunar sojin Kamaru wanda ba ta amince a bayyana sunanta ba, ta shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin cewa, maharan sun kaddamar da harin ne a wani sansanin sojojin Kamaru dake Soueram, a yankin arewa mai nisa wanda ke iyaka da Najeriya, lamarin dai ya faru ne da misalin karfe 2 na daren Asabar, agogon yankin, sai dai dakarun sojin sun yi nasarar dakile wannan hari.

A binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa, 7 daga cikin maharan ne aka tsinci gawawwakinsu a wajen. Majiyar ta kara da cewa Kamarun ta yi hasarar biyu daga cikin sojojinta a lokacin wannan harin.

Sai dai kawo yanzu babu wata kungiya da ta yi ikirarin kai harin, kana babu wasu bayanai da hukumomin Jamhuriyar Kamaru suka fitar game da wannan hari.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China