in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Nijeriya ta ceto mutane 211 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
2017-03-13 09:57:27 cri

Dakarun rundunar sojin Nijeriya dake aiki a jihar Borno a yankin arewa maso gabashin kasar, sun ceto mutane 211 da kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da su.

Wata sanarwa da kakakin rundunar Sani Usman ya fitar, ta ce dakarun runduna ta 22 ta Garrison dake aiki karkashin shirin Operation Lafiya Dole, sun ceto mutanen ne yayin wani samame da suka kai kauyukan Cingal Murye da Maja a ranar Asabar.

Nijeriya ta samu nasara a yakin da take da kungiyar Boko Haram, inda a watan Disamban bara, dakarunta dake aiki a yankin arewa maso gabashin kasar suka fatattaki mayakan kungiyar daga dajin Sambisa wanda shi ne sansanin kungiyar mafi girma a kasar.

Jami'an tsaro sun kara matse kaimi wajen aikin sintiri a yankin, inda suka fadada ayyukan na su zuwa iyakokin Niger da Chadi.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China