in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin ya bukaci bangarorin Syria su aiwatar da yarjejeniyar tsakaita bude wuta
2017-01-01 12:19:43 cri
A jiya Asabar jakadan kasar Sin ya bukaci gwamnatin Syria da kungiyoyi masu adawa da gwamnatin yanzu da su amince da aiwatar da yarjejeniyar tsakaita bude wuta yadda ya kamata wanda kasashen Rasha da Turkiyya suka gabatar.

Wu Haitao, wanda shi ne mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD, ya yi wannan kira ne bayan da kwamitin tsaro na MDD ya kada kuri'ar goyon bayan shirin yarjejeniyar tsakaita bude wutar, da kuma sabon shirin tattaunawar zaman lafiya a tsakanin bangarorin da ba sa ga maciji da juna, wanda ake sa ran gudanarwa a Astana, babban birnin Kazakhstan.

Wu ya ce kasar Sin tana maraba da sanya hannu kan yarjejeniyar tsakaita bude wutar, kana ta yaba da ci gaban da aka samu game da sakamakon da aka cimma dangane da bijirewa da kasashen Rasha da Turkiyya suka yi a baya. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China