in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu sakamakon zaftarewar laka a wajen zubar da shara a Habasha ya karu zuwa 35
2017-03-13 09:05:38 cri
Rahotanni daga Addis Ababa na kasar Habasha na cewa, yawan mutanen da suka mutu sakamakon zaftarewar laka a wajen wani babban jujin zubar shara a wajen Addis Ababa na kasar Habasha ya karu zuwa 35.

Shugaban ofishin hulda da jama'a na birnin Addis Ababa Dagmawit Moges ya bayyana cewa, adadin mutane da suka mutu yana iya karuwa yayin da ake ci gaba da aikin zakulo wadanda suke da sauran numfashi a wurin da bala'in ya faru.

A ranar Asabar da dare ne dai tabo da sauran tarkace suka gangaro daga babban wurin zubar da sharar da aka kwashe shekaru kusan hamsin ana amfani da shi, lakar da ta gangaro ta rufe gidaje baya ga wasu mazauna wurin da dama da ake fargabar sun bace.

Magarin garin birnin Addis Ababa Diriba Kuma, ya shaidawa manema labarai a jiya Lahadi da safe cewa, ana ci gaba da gudanar da ayyukan ceto tare da neman mutanen da suka bace tun lokacin aukuwar lamarin da misalin karfe 8 na daren ranar Asabar agogon wurin. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China