in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Habasha zasu karfafa dangantakar dake tsakaninsu domin samun cigaba
2016-11-19 12:46:19 cri
Kasashen Sin da Habasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyar cigaba da yin musayar dabaru tsakanin jam'iyyun dake jan ragamar kasashen biyu.

A lokacin ziyarar aiki da ya kai Habasha, mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao, ya ce Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin wato CPC, da jam'iyyar Ethiopian People's Revolutionary Democratic Front (EPRDF), sun gudanar da musayar dabaru na hadin gwiwa da kuma karawa juna sani

Da yake zantawa da mataimakin Firaiministan kasar Habasha Demeke Mekonnen, wanda kuma shine mataimakin shugaban jam'iyyar ta EPRDF, Li, ya bukaci a kara zurfafa dangantaka da musayar kwarewa a tsakanin bangarorin biyu, domin samun gagarumin cigaba ta fuskar kyakkywar mu'amala dake tsakanin kasashen biyu.

Ya kara da cewa, jam'iyyar CPC ta kasar Sin da gwamnatin Sin, za su aiwatar da sakamakon da aka cimma a lokacin taron dandalin hadin kan Sin da Afrika wato (FOCAC), wanda ya gudana a watan Dismabar bara a birnin Johannesburg, wanda hakan zai taimaka wajen cigaban tattalin arziki da zamantakewar al'ummar kasar Habasha.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China