in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Habasha ta kama wadanda ake zargi da tada zaune-tsaye fiye da dubu 10
2016-11-13 13:18:55 cri
Hukumar bincike kan halin dokar-ta-bace ta kasar Habasha ta bayar da sanarwa a ranar 12 ga wata cewa, bayan da aka sanar da shiga halin dokar-ta-bace, an riga an kama mutanen da ake zargi da aikata laifuffukan tada zaune-tsaye fiye da dubu 11 da dari 6, ciki har da mata 347.

Sanarwar ta bayyana cewa, ana zarginsu da aikata laifuffukan janyo barazana ga gwamnatin kasar Habasha, ciki har da tsara da tada rikici, lalata gine ginen gwamnati, raunata fararen hula da jami'an tsaron kasar da dai sauransu.

A kwanakin baya, an yi rikici a tsakanin 'yan kabilar Oromo dake yankin Oromia na kasar da gwamnatin kasar kan batun mayar da filaye a hannun gwamnati, lamarin da ya janyo zanga-zanga a yankin, da tayar da rikici tsakanin mazauna wurin da 'yan sanda, wanda ya haddasa mutuwar mutane da dama, da tsananta halin da ake ciki a yankin.

A ranar 9 ga watan Oktoba, gwamnatin kasar Habasha ta sanar da ayyana dokar-ta-bace har na tsawon watanni 6 a kasar don tabbatar da kwantar da hankali. Ban da wannan kuma, an kyautata membobin gwamnatin kasar, da kara yawan kujeru ga 'yan kabilar Oromo domin kwantar da damuwar 'yan kabilar Oromo din. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China