in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Layin dogo da kamfanin Sin ya gina a Habasha zai bunkasa tattalin arzikin kasar inji wani jami'i
2016-10-06 11:54:19 cri
Mashawarci na musamman ga firaministan kasar Habasha Arkebe Oqubay, ya bayyana cewa layin dogo da ya hade Habasha da kasar Djibouti, wanda kamfanin kasar Sin ya gina, zai yi matukar tallafawa aniyar kasar sa a fannin bunkasa tattalin arziki.

Mr. Oqubay wanda ya shaida hakan ga kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, ya kara da cewa aikin zai kuma fadada cin gajiyar kasashen biyu a bangaren musayar fasahohin sufuri na zamani. Kaza lika zai bunkasa harkokin shige da ficen hajoji da inganta ci gaban masana'antu a kasar ta Habasha.

Jami'in ya ce baya ga wadannan manyan damammaki da kasar za ta samu, sabon layin dogon zai kuma karfafa kawance, da hadin gwiwa dake tsakanin Habasha da kasar Sin.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China