in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a karrama tsohon shugaban kasar Ghana a Afirka ta kudu
2017-02-23 20:52:01 cri
Yanzu haka tsohon shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama yana kasar Afirka ta kudu, inda za a karrama shi da lambar yabo ta shugaban da ya yi fice a harkokin siyasa na wannan shekara.

Wata sanarwar da mai tallafawa tsohon shugaban kasar Ghana Joyce Bawah Mogtari ta bayar ta ce, mujallar dake sharhi kan harkokin shugabanci a Afirka(ALM) wadda ta shirya bikin ta ce, akan zabi mutumin da ya lashe kyautar ce bisa la'akari da rawar da ya taka wajen kare martabar nahiyar a idon duniya, tare da nuna shugabanci na gari gami da gudummawar da ya ba da ga ci gaban nahiyar Afirka.

Mujallar ta ce an zabi Mahama ne saboda gudummawar da ya ba da ga ci gaban harkokin demokiradiya a kasar Ghana.

Baya ga wannan lambar yabo, za kuma a baiwa Mahama takardar yabo ta kungiyar 'yan majalisun dokoki bakaken fata daga Georgie a yayin wannan biki.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China