in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Dan jaridar Kenya: Fasahohin da Sin ta samu wajen kawar da talauci sun cancanci koyi ga kasashen Afirka
2017-03-06 16:03:04 cri
An bude zaman taro karo na 5 na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 12 da safiyar jiya Lahadi, inda firaministan kasar Li Keqiang ya jagoranci rahoton ayyukan gwamnati.

Game da wannan, 'dan jaridar rediyon kasar Kenya Eric Biegon ya bayyana wa 'yan jaridun gidan rediyon kasar Sin CRI cewa, fasahohin da kasar Sin ta samu wajen kawar da talauci, sun cancanci kasashen Afirka su yi koyi da su.

Eric Biegon ya kara da cewa, a cikin rahoton an gabatar da cewa, kamata ya yi a gudanar da ayyukan kawar da talauci bisa halin musamman, kuma a bana kasar Sin za ta kara rage matalauta sama da miliyan 10 a kauyuka. Wannan ya nuna cewa, gwamnatin kasar Sin ta mayar da hankali sosai kan shawarwarin da wakilai bisa matsayi daban daban na kasar suke gabatarwa game da yadda ake kokarin rage matalauta a birane da kauyuka, da kara samar da guraban aikin yi, da kuma inganta kyautatuwar zaman rayuwar jama'a. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China