Kakakin gwamnatin kasar, Philippe Nzobonariba ne ya bayyana haka lokacin da yake gabatar da sakamakon taron majalisar zartaswar kasar na makon jiya.
A bara, gudumomi da dama na kasar sun fuskanci matsalar fari, al'amarin da ya yi mummunar tasiri ga yawan abincin da kasar ta sa ran samu.
A cewar Philippe Nzobonariba, nan ba da dadewa ba, za a sanar da jerin kayayyakin abincin da aka dage musu haraji. (Fa'iza Mustapha)