in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burundi ta kaddamar da shirin afuwa ga fursunonin siyasa
2017-01-24 10:47:11 cri
A jiya Litinin Burundi ta kaddamar da shirin yafiya ga fursunoni 2,500 a kasar, cikinsu har da fursunonin siyasa, bayan matakin yin afuwa da shugaban kasar ya dauka.

Ministar shara'a ta kasar Burundin Aimee Laurentine Kanyana, ita ce ta kaddamar da shirin a gidan yari na Mpimba dake Bujumbura babban birnin kasar.

Wannan afuwar da shugaban kasar Burundin Pierre Nkurunziza ya yi, ya sanar da yinta ne a cikin jawabinsa na sabuwar shekara.

Ministar ta ce daga cikin wadanda aka yiwa afuwar akwai mutane 58 daga jam'iyyar hamayya ta (MSD). Haka zalika, cikin wadanda afuwar ta shafa akwai 'yan ta da kayar baya da suka shiga zanga zangar nuna adawa da takarar shugaba Nkurunziza a watan Afrilun shekarar 2015.

Madam Aimee tace wadanda afuwar shugaban kasar ta shafa su ne mazauna gidajen yarin da laifukansu ba su kai daurin shekaru biyar ba, da kuma wadan da suka shafe kashi 3 bisa kashi 4 daga cikin adadin shekarun da aka debar musu, kana mutanen dake nuna halin da'a yayin da suke cikin kurkuku.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China