in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan Burundi sun yi zanga zangar kin amincewa da rahoton majalisar Turai game take hakkin dan Adam
2017-01-29 13:17:22 cri
Dubban jama'a a kasar Burundi sun fita kan tituna a jiya Asabar domin yin zanga zangar kin amincewa da wani rahoto da majalisar dokokin Turai ta fitar game da take hakkin bil adama a kasar ta gabashin Afrika.

Da yake karanta jawabin gwamnatin Burundi, mataimakin ministan harkokin cikin gida Therence Ntahiraja ya ce, suna kira ga shugabannin kungiyar tarayyar Afrika (AU) dake taro a Habasha a ranar 31 ga watan nan, da MDD da su yi watsi da rahoton da majalisar dokokin Turai ta fitar wanda babu komai cikinsa sai karairayi da ruruta wutar rikici da kuma jita jita.

Wannan zanga zanaga an gudanar da ita a duk fadin kasar, kuma jami'an gwamnatin kasar sun bi sahun jama'a don gudanar da zanga zangar.

A ranar 19 ga watan Janiru ne, majalisar dokokin Turai ta gabatar kuduri inda ta nuna wasu batutuwa da suka shafi cin zarafin bil adama a kasar Burundin.

To sai dai kuma, gwamnatin kasar Burundi, da majalisar dokokin kasar sun yi watsi da wannan rahoto, inda suka bayyana shi da cewa garyace tsagwaronta. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China