in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta mai da hankali kan inganta tattalin arziki da kwanciyar hankalin al'umma a shekarar 2017
2017-03-05 11:31:59 cri
Firayin ministan Kasar Sin Li Keqiang, ya ce a bana, kasar za ta rubanya kokarinta wajen ganin ta samar da ci gaba tare da tunkarar duk wata barazana, da nufin samun dorewar tattalin arzikinta da kwanciyar hankalin al'umma.

Da yake gabatar da rahoton ayyukan gwamnatin kasar ga taron wakilan jama'ar kasar, Li Keqiang, ya ce samar da kwanciyar hankali na da muhimmanci gaya, inda ya ce dole ne a kiyayi kai wa matakin gargadi na rashin kudi, tare da tabbatar da kare muhalli da zamantakewar al'umma.

Rahoton ya ce a kokarinta na cimma wadannan muradu, kasar Sin za ta matse kaimi wajen aiwatar da sauye-sauye da za su kai ta ga samun nasarori a muhimman bangarori. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China