in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta yi fatali da rahoton kungiyar Amnesty
2017-02-28 09:34:43 cri
Kakakin rundunar tsaron Najeriya Birgediya Janar Rabe Abubakar, ya karyata rahoton da kungiyar kare hakkin bil adama ta kasa da kasa wato Amnesty International ta fitar, wanda ke zargin, sojojin Najeriyar da hallaka fararen hula 240, ciki hadda jarirai a jihar Borno, da kuma wasu mutanen su 177 dake fafutukar kafuwar kasar Biafara.

Da yake mai da martani game da rahoton a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai Rabe Abubakar, ya ce rahoton na Amnesty shirme ne kawai. Ya ce, yana fatan al'umma za su yi fatali da shi, ganin cewa, a baya ma kungiyar ta Amnesty, ta sha fidda irin wannan rahoto, inda take zargin sojoji da sauran jami'an tsaron kasar da aikata laifuka, ba tare da wata hujja mai karfi ba.

Kaza lika Rabe ya zargi Amnesty International da kitsa bayanai marasa kan gado domin cimma wata manufa ta daban, da kuma yunkurin haifar da rashin hadin kai da tsana tsakanin 'yan Najeriya.

A hannun guda kuma gwamnatin Najeriyar ta ce ba ta ji dadin yadda kungiyar Amnesty wadda ya kamata a ce ta tsame kanta daga harkokin siyasa, sannan ta rika ba da rahoto ba tare da nuna son kai ba, amma ita ce ta ke irin wannan katubara.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China