in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta sassauta ka'idojin neman Visa ga masu sha'awar kasuwanci da yawon bude ido
2017-02-27 09:57:41 cri
Ministan watsa labarai da al'adu na tarayyar Najeriya Lai mohammed ya ce gwamnatin Najeriyar ta sassauta ka'idojin neman takardar iznin shiga kasar wato Visa ga bakin da ke sha'awar shiga kasar da nufin gudanar da harkokin kasuwanci ko yawon shakatawa.

Ministan wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwar da aka rabawa manema labarai a birnin Legas, ya ce an dauki wannan mataki ne da nufin kawar da duk wani shige da masu sha'awar yin harkokin kasuwanci da yawon shakatawa a cikin kasar ke fuskanta, ta yadda hakan zai bunkasa tattalin arzikin kasar.

Minista Lai ya kara da cewa, wannan wani bangare ne cikin jerin matakan da gwamnati ta tsara da nufin saukaka harkokin kasuwanci da bunkasa yawon bude ido, karkashin shirin mahukuntan kasar na fadada sassan tattalin arzikinta.

Yanzu haka dai hukumar shige da ficen kasar (NIS) ta fara nazartar ka'idojin samun takardar iznin shiga kasar, a wani mataki na fara janyo masu sha'awar gudanar da huldar arziki a cikin kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China