in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya na fuskantar kalubale a sassan da suka sha fama da tashe tashen hankula
2017-02-24 09:25:24 cri
Ministan tsaron tarayyar Najeriya Mansur Dan-Ali, ya bayyana cewa kasar na fuskantar dumbin kalubale a fannoni da dama, musamman a yankunan arewa maso gabashin kasar, inda aka sha fama da tashe tashen hankula.

Ministan ya bayyana hakan ne a yayin wani taro na masu ruwa da tsaki, wanda gamayyar kafofin watsa labaru na nahiyar Afirka suka shirya, game da ayyukan tada kayar baya, taron da ya gudana a Abuja fadar mulkin kasar.

Mansur Dan-Ali ya ce yana farin ciki da ganin yadda kungiyoyi masu zaman kan su ke maida hankali, wajen magance tarin matsaloli da wannan yanki ya fuskanta ta fuskar tsaro da yaki da ta'addanci da dai sauran su.

Daga nan sai ya ja hankulan matasa da jam'iyyun gama kasar a kasar, da su sauke nauyin dake wuyan su, na tabbatar da zaman lafiya da ci gaba mai dorewa a dukkanin fadin kasar.

Ya ce yayin da gwamnati ke hankoron ganin ta cimma nasarar wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkanin sassan Najeriya, kamata ya yi 'yan kasar su ma, su kauracewa duk wani mataki daka iya haifar da tada husuma, ko kuma yiwa dokokin kasar karan tsaye.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China