in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban hafsan tsaron Nijeriya ya ce dakarun hadin gwiwa sun karya lagon kungiyar Boko Haram
2017-02-22 10:22:29 cri
Babban hafsan tsaro na Nijeriya, ya ce an samu raguwar ayyukan 'yan ta da kayar baya a kasar, yana mai yabawa kokarin kasashen dake cikin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF da ta kunshi dakarun kasashen yankin Tafkin Chadi da Benin.

Abayomi Olonisakin ya bayyana haka ne jiya a Abuja, yayin bude wani taron yini uku na kwararru daga kasashe mambobin hukumar kula da yankin Tafkin Chadi da Benin.

Ya kuma bukaci rundunar hadin gwiwar ta kara zage damtse wajen murkushe ragowar 'ya'yan kungiyar Boko Haram.

A cewarsa, fatattakar 'yan ta da kayar bayan daga maboyarsu a Nijeriya, ya sa sun bazu, inda suke kai hare-hare yankunan dake karkashin ikon rundunar.

Olonisakin ya ce wannan yunkuri ne na 'yan tada kayar bayan na sake haduwa.

Babban hafsan tsaron ya ce kowace kasa cikin kasashen yankin na amfani da nata dabarun yaki da ta'addanci, sannan kuma suna daukar wasu matakai a tare, yayin da yakin na sojoji ke ci gaba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China