Da yake tsokaci game da hakan a birnin Abuja fadar mulkin kasar, gwamna Bello, ya ce an cafke mayakan Boko Haram din ne a shekaranjiya Litinin, ana kuma zaton 'ya'yan kungiyar na yunkurin sake taruwa ne a jihar, bayan da dakarun sojin kasar suka fatattake su daga yankin arewa maso gabashin kasar.
Sai dai fa gwamnan na jihar ta Kogi ya ce masu tada kayar bayan sun makara, domin kuwa gwamnatinsa, da hadin kan sassan jami'an tsaron kasar, za su yi duk mai yiwuwa, wajen tabbatar da cewa hakar su bata cimma ruwa ba.
Daukar wannan mataki ko shakka babu, zai tabbatar da nasarar da dakarun sojin Najeriya suka samu a yakin da suke yi da 'yan Boko Haram a arewa maso gabashin kasar, kamar dai yadda gwamnan ya bayyana. (Saminu Hassan)