Bayanai na nuna cewa, sojojin da dakarun suka kashe, sojojin kota-kwana ne wadanda aka girke a wani sansanin ba da horon soja dake kusa da babban birnin kasar, Niamey. Kuma suna kan hanyarsu ce ta koma wa sansaninsu a lokacin da aka kai musu harin.
Ya zuwa tsakar ranar jiya dai, gwamantin Nijer din ba ta yi wani karin bayani game da harin da ya auku ba, kuma babu wata kungiya da ta sanar da daukar alhakin kai harin. (Maryam)