Bisa labarin da kafofin watsa labaru na jamhuriyar Nijer suka bayar a jiya Asabar an ce, dakarun kungiyar Boko Haram sun kai hari ga wani sansanin soja na jihar Diffa dake kudu maso gabashin kasar a safiyar ranar Asabar, wanda ya haddasa mutuwar sojojin kiyaye tsaron kasar a kalla 2, tare da raunukar mutane 3.
An ce, an kai harin ne a sansanin dake kan iyakar kasashen Nijer da Nijeriya. A halin yanzu, sojojin gwamnatin jamhuriyar Nijer suna yunkurin kama maharan. (Zainab)