A kwanan baya ne, aka kaddamar da wani littafi mai kunshe da zababbun takardun da aka gabatar a taron kolin shugabannin kasashen kungiyar G20 da ya gudana a birnin Hangzhou na kasar Sin.
Shi dai wannan litattafi, ana sayar da na Sinancinsa a nan kasar Sin yayin da ake sayar da wanda aka fassara cikin harshen Turanci a kasashen waje.
An samu nasarar gudanar da taron kolin G20 karo na 11 a watan Satumban bara ne a birnin Hangzhou, inda aka samu sakamako da dama, wadanda ba a taba ganin irinsu a baya ba. Taron ya kuma tsara ajandar bunkasa tattalin arzikin kasa da kasa, ya kuma sanya halin musamman na kasar Sin kan yadda za a farfado da tattalin arzikin duniya. (Tasallah Yuan)