in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin zai halarci wasu tarukan kasa da kasa a Jamus
2017-02-14 19:42:57 cri

Ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a Talatar nan cewa, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, zai kai ziyara kasar Jamus tsakanin ranekun 15 zuwa 18 ga watan nan, domin halartar kwarya-kwaryar taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar G20, da kuma taron Munich game da harkokin tsaro.

Ana dai fatan tattauna yadda za a aiwatar da shirin samun ci gaba mai dorewa na shekarar 2030, da batun kiyaye zaman lafiya, da inganta huldar abokantaka da kasashen Afirka, a yayin kwarya-kwaryar taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar G20 na wannan karo. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China