in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron ministocin harkokin wajen kasashen G20 a Jamus
2017-02-17 11:11:34 cri
Jiya Alhamis ne, aka fara wani taron yini biyu na ministocin harkokin wajen kasashen G20 a birnin Bonn na kasar Jamus, inda mahalarta taron za su tattauna kan manyan batutuwa uku da suka hada da aiwatar da shirin jadawalin maradun ci gaba mai dorewa da ake son cimmawa kawo shekarar 2030, da wanzar da zaman lafiya da kuma inganta dangantaka da kasashen nahiyar Afirka, a wani bangare na shirye-shiryen taron kolin G20 da za a yi a birnin Hamburg a watan Yulin bana.

Tuni dai kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya shaidawa manema labarai cewa, kasar Sin na fatan wannan taro, zai mai da hankali wajen karfafa hadin-gwiwa, da tunkarar manyan kalubalen da kasashe da dama ke fuskanta, tare da kara daidaita harkokin duniya, da kuma raya tattalin arzikin duniya ta hanyar da ta dace, wadanda batutuwa ne dake da matukar muhimmanci ga kasashe daban-daban a halin yanzu.

A cikin wata sanarwar da ya fitar gabannin taron, mataimakin firaministan kasar Jamus, kana ministan harkokin wajen kasar, Mista Sigmar Gabriel ya bayyana cewa, yana fatan taron ministocin harkokin wajen kasashen G20 gami da taro karo na 53 kan harkokin tsaro da za a yi nan ba da jimawa ba a birnin Munich, za su tattauna kan matakan da kasashe za su dauka na tunkarar manyan kalubale a fadin duniya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China