in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani harin kunar bakin wake ya raunata 'yan sanda uku a gabashin Aljeriya
2017-02-27 09:39:06 cri
Rahotanni daga kasar Aljeriya na cewa, wasu 'yan sanda uku sun jikkata lokacin da wani dan kunar baki wake ya tarwatsa kansa a kusa da wani ofishin 'yan sanda dake garin Bab el Kantara a gabashin lardin Constantine.

Shafin intanet na TSA ya ba da labarin cewa, wani dan sanda ne ya budewa dan kunar bakin waken wuta a lokacin da ke kokarin tayar da bam din dake jikinsa a wajen ofishin 'yan sanda. Bayan dan kunar bakin waken ya fadi kasa ne kuma sai nan da nan ya tayar da bam din da ke makale a jikinsa, inda ya kashe kansa kana ya jikkata wasu jami'an 'yan sanda uku.

Sai dai jim kadan bayan kai wannan hari, mahukuntan kasar suka tura rukunin yaki da ayyukan ta'addanci zuwa wurin da lamarin da ya faru.

Kasar Aljeriya dai tana ci gaba da fuskantar barazanar ta'adddanci, sakamakon matsalar tsaro da rigingimun siyasa da yankin ke fuskanta. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China