Wata sanarwar da majalisar tsaro ta jihar ta fitar jiya, ta ce an dauki matakin ne domin kare rayuka da dukiyoyi, da kuma kare sake barkewar rikici a lardunan Kaura da Jema'a, inda rikici ya barke a ranar Lahadi ya kuma ci gaba har zuwa Litinin.
Gwamnatin Jihar ta ce an umarci dukkan hukumomin tsaro su tabbatar da kiyaye dokar.
Duk da kokarin hukumomin Nijeriya na sulhunta bangarorin da ke rikici da juna, tsawon watanni, tsakanin makiyaya da al'ummomin yankin Kaduna ta Kudu yaki ci-ya-ki cinyewa. (Fa'iza Mustapha)