in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Muhimman labarai daga wasu jaridun Najeriya
2017-02-21 19:21:04 cri
Bisa labarin da jaridar Daily Trust ta wallafa, an ce, majalisar dattawan Najeriya ta bukaci hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasar ta'annati, da ta mayar da hankalin wajen farautar wasu manyan jami'an babban bankin kasar(CBN) wadanda majalisar ta kira manyan masu kudin kasar.

Sannan jaridar Vanguard ta Najeriya ta bayar da labara cewa, babban bankin Najeriya (CBN) ya fito da wasu sabbin matakan canjin kudaden ketare, a wani mataki na rage matsin lambar da kudin kasar wato Naira yake fuskanta kan yadda ake musayarsa a kasuwar bayan fage a halin yanzu.

Amma kuma duk da sabbin matakan da babban bankin Najeriyar ya bullo da su, yanzu haka ana sayan kowace dalar Amurka daya kan Naira 520 a kasuwar bayan fage.

Bugu da kari, jaridar "The Guardian" ta Najeriya ta labarta cewa, kungiyar kwadago a Najeriya ta yi Allah wadai da shirin da mahukuntan kasar Najeriya ke yi na sallamar ma'aikata 3,500 daga aiki, kan abin da gwamnatin ta ce an dauke su ne ba bisa ka'ida ba. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China