in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bada Lambar yabo ga 'yan sandan kasar Sin dake aikin wanzar da zaman lafiya a Liberia
2017-02-22 10:01:30 cri
Ma'aikatar tsaron al'umma ta kasar Sin, ta ce shirin MDD mai wanzar da zaman lafiya a Liberia, ya ba da lambar yabo ga 'yan sandan kasar Sin, saboda iri rawar da suka taka wajen wanzar da zaman lafiya a kasar Liberia.

Yayin wani biki da ya gudana a Monrovia babban birnin Liberia, MDD ta bada lambar yabo na wanzar da zaman lafiya ga jimilar 'yan sandan kasar Sin dari da arba'in, wato tawagar 'yan sandan kwantar da tarzoma na kasar Sin na hudu, da aka tura Liberia tun watan Satumban 2013.

Tawagar 'yan sandan ta bar kasar Sin a watan Maris din 2016 domin aikin tsawon shekara guda, inda aka dora mata nauyin tabbatar tsaro a Monrovia. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China