in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ellen Johnson-Sirleaf ta gana da rundunar 'yan sandan Sin dake Liberiya
2016-05-01 17:12:34 cri

A jiya ranar 30 ga watan Afrilu, shugabar kasar Liberia Ellen Johnson-Sirleaf ta gana da rundunar 'yan sandan kiyaye zaman lafiya ta hudu dake kasar Liberia a birnin Monrovia, inda ta yabawa aikin rundunar game da gudummawar da ta samar sosai wajen tabbatar da zaman lafiya da samun bunkasuwa a kasar Liberia.

A yayin ganawar, madam Sirleaf ta bayyana cewa, jama'ar kasar Sin abokan jama'ar kasar Liberia ne, tare da nuna godiya ga gwamnatin kasar Sin game da goyon baya da taimako da take kawowa ga kasar wajen kiyaye zaman lafiya da samun bunkasuwa. Jama'ar kasar Liberia suna maraba da zuwan rundunar 'yan sandan kiyaye zaman lafiya na kasar Sin, da nuna godiya gare su bisa kokarin da suke yi na gudanar da ayyukansu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China