in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Uganda da babban sakataren MDD sun yi kira da a kawo karshen rikici a Sudan ta kudu
2016-07-17 13:14:39 cri
Shugaban kasar Uganda Yoweri Museveni da babban sakataren MDD mista Ban Ki-moon sun yi kira ga masu ruwa da tsaki a Sudan ta Kudu da su kawo karshen zaman doya da manja dake tsakanin bangarorin kasar.

Cikin wata sanarwar da aka gabatar daga birnin Kampala na kasar Uganda, shugaba Museveni da Mista Ban sun ce, shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir da mataimakinsa Riek Machar sun gaza mutunta cikakken goyon bayan da bangarorin kasa da kasa suke nunawa wannan jaririyar kasa.

Museveni ya ambaci abubuwa 3 masu mumimmanci da ya kamata a lura da su a halin yanzu, da suka hada da kafa wata rundunar kiyaye zaman lafiya a yanki, da tsagaita bude wuta a Juba, gami da kaddamar da babban zabe da maido da tsarin dimokuradiya a kasar cikin gaggawa.

A nasa bangaren, Ban ya ce yadda shugabannin 2 na Sudan ta Kudun suka yi watsi da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ya sa MDD cikin wani mawuyacin hali, don haka ya yi kira ga shugaba Museveni, wanda shine mai shiga tsakani, da ya yi kokari tare da kungiyar AU da sauran bangarorin yankin don nuna kin amincewa da sake barkewar yaki a kasar a nan gaba.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China