in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci a kara kokari wajen samar da ayyukan yi a bana
2017-02-18 12:36:53 cri
Mataimakin firayin ministan kasar Sin Ma Kai, ya bukaci a kara kokari wajen ba batun samar da aikin yi muhimmanci a bana.

Ma Kai ya yi wannan kira ne yayin taron majalisar gudanarwar kasar, inda ya ce, har yanzu kasar na fuskantar matsala game da ayyukan yi, al'amarin da ya ce akwai bukatar hukumomi su kara zage damtse wajen shiryawa da tsara yadda za a magance matsalar.

Ya ce akwai bukatar bunkasa ayyukan masana'antu da kamfanoni ta yadda za a samar da karin guraben aikin yi, da karfafawa mutane fara sana'a a kansu, tare da ba da horo kan sana'o'in hannu.

A bara dai, kasar Sin ta samar da guraben aikin yi miliyan 13.1 ga mazauna birane. Duk da haka, zuwa karshen shekarar, adadin marasa aikin yi dake da rajista a biranen kasar ya kai kashi 4 cikin dari. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China