in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: Ba wata dabara ta daban baya ga kudurin samar da kasashen biyu
2017-02-16 13:41:08 cri
Sakatare janar na MDD Antonio Guterre, ya fadawa taron manema labarai a bayan wata ganawa da ya yi da shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi, cewa babu wani zabi da wuce kudurin samar da kasashen biyu, wato Isra'ila da Palestinu, duba da cewa hakan ne kadai zai tabbatar da warware rikicin gabas ta tsakiya, kana ya tabbatar da kwanciyar hankali a wannan shiyya.

Jawabin na mista Guterres ya zo ne, bayan wasu kalamai da shugaban Amurka Donald Trump ya yi a birnin Washington, a lokacin taron manema labarai tare da firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, inda ya ce shirin samar da kasashen biyu, ba shi kadai ne mafita ba, saboda irin rashin adalcin da MDDr take yiwa kasar Isra'ila.

Babban sakataren MDD ya jaddada kalaman nasa a wata lacca da ya gabatar, a jami'ar birnin Cairo, wadda ta samu halartar jami'an diplomasiyya da dalibai.

Guterres, ya bayyana rikici tsakanin Isra'ila da Palestinu, wanda aka shafe gwamman shekaru ana yi, a matsayin tushen rikicin shiyyar baki daya.

Ya ce dole ne a dauki kwararan matakai domin warware rikicin kasashen biyu da ya ki ci ya ki cinyewa, ya kara da cewa kasar Masar ita ce babbar jagora wajen warware duk wata takaddama da ta shafi yankin gabas ta tsakiya. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China