in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a soke haramcin gina matsugunan Yahudawa dake gabashin birnin Kudus
2017-01-23 13:46:56 cri

A jiya ne firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana a taron majalisar tsaron kasar cewa, za a soke haramcin da aka yi game da gina matsugunan Yahudawa dake gabashin birnin Kudus.

Sai kuma wata sanarwa da fadar shugaban Palesdinu ta fitar, ta yi Allah wadai da matakin Isra'ila na ba da iznin gina matsugunan Yahudawa a gabashin birnin Kudus, inda ta kalubalanci kasashen duniya da su matsawa Isra'ila lamba ta martaba kudurin MDD kana ta gaggauta yin watsi da shirinta na gina matsugunan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China