in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dokar gina matsugunan Yahudawan Isra'ila ta sabawa dokar kasa da kasa, in ji Guterres
2017-02-08 10:53:32 cri
Babban magatakardan Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya fitar da wata sanarwa a jiya Talata ta bakin kakakinsa, inda ya nuna rashin jin dadi game da dokar da kasar Isra'ila ta bullo da ita, wadda ta amince da matsugunan da wasu Yahudawa suka gina ko za'a gina a yankunan Falasdinawa dake yammacin kogin Jordan ba tare da izni ba. Guterres ya nuna cewa, wannan doka ta sabawa dokar kasa da kasa, za kuma ta yi babban tasiri ga Isra'ila ta fuskar doka.

Shekaran jiya Litinin ne majalisar dokokin kasar Isra'ila ta zartas da wani shirin doka, wanda ya amince da matsugunan da wasu Yahudawa suka gina ko za'a gina a yankunan yammacin kogin Jordan ba tare da izni ba.

Shima a nasa bangaren, shugaban al'ummar Falasdinawa Mahmoud Abbas ya ce, wannan doka da majalisar dokokin Isra'ila ta amince da ita, ta keta dokokin kasa da kasa.

A wani labarin kuma, kasashen Jordan da Masar sun fitar da sanarwa a jiya Talata, inda suka yi tofin Allah tsine game da shirin dokar da Isra'ila ta amince da shi.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China