in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba za ta amince da duk wata kasar da za ta kawo illa ga 'yancin mallaka da tsaron kasar Sin bisa dalilin 'yancin yin zirga-zirga ba
2017-02-16 11:16:25 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a gun taron manema labaru a jiya Laraba cewa, Sin tana girmama tare da tabbatar da 'yancin yin zirga-zirga a yankin tekun kudancin Sin kamar yadda dokokin kasa da kasa suka tanada. Amma kuma Sin ba za ta amince wata kasa da take mata 'yancin mallaka da tsaron kasarta ba ta hanyar facewa da 'yancin yin zirga-zirga.

Game da shirin da sojojin ruwa na kasar Amurka ke yi na tura jirgin yaki na ruwa samfurin USS Carl Vinson CVN-70 zuwa yankin tekun kudancin Sin don tabbatar da 'yancin zirga-zirgar jiragen ruwa, kana sun ce watakila za su shiga tekun dake dab da tsibirorin dake yankin, Geng Shuang ya bayyana cewa, tekun kudancin Sin da sauran tsibiran dake yankin mallakar kasar Sin ne. A saboda haka, ya kalubalanci kasar Amurka da ta guji daukar matakan da za su kawo illa ga 'yancin mallaka da tsaron kasar Sin, maimakon haka, kamata ya yi Amurkar ta girmama kokarin da kasashen dake yankin suke yi na tabbbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin baki daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China