in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Sin da Amurka sun tattauna da juna ta waya ne bisa shirin da suka cimma daidaito
2017-02-10 20:35:46 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Jumma'a cewa, yau da safe shugabannin kasashen Sin da Amurka sun tattauna da juna ta waya bisa shirin da suka cimma daidaito. Shugabannin suna fatan za su gana da juna cikin hanzari, tare da kiyaye yin mu'amala da juna game da ganawar da shugabannin kasashen biyu za su yi a nan gaba.

Lu Kang ya bayyana cewa, manufar Sin daya tak a duniya ita ce babban ginshikin raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, wadda ta tabbatar da raya dangantakar yadda ya kamata. Sin tana fatan kasar Amurka za ta warware batun yankin Taiwan yadda ya kamata ta hanyar martaba manufar Sin daya tak a duniya da hadaddiyar sanarwa guda uku da Sin da Amurka suka bayar tare, wannan zai taimaka wajen tabbatar da ci gaba da yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

Game da batun ko za a kara yin mu'amala da hadin gwiwa a tsakanin Sin da Amurka bayan da shugabannin biyu suka tattauna da juna ta waya, Lu Kang ya bayyana cewa, a matsayinsu na manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya, kuma daya kasa ce mai tasowa mafi girma a duniya, yayin da dayan kuma kasa ce da fi ci gaba a duniya, akwai bukata da Sin da Amurka su fadada hadin gwiwarsu a fannoni da dama. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China