in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwararru a fannin kiwon lafiya sun yi kira da karin hadin gwiwa domin inganta harkokin lafiya a Nahiyar Afrika
2017-02-14 10:15:39 cri
A jiya Litinin ne kwararru daga kamfanonin hada magunguna daban-daban na nahiyar Afrika, suka yi kira da samar da hadin gwiwa tsakanin gwamnatoci da bangarori masu zaman kansu, da nufin inganta harkokin kiwon lafiya a yankin kudu da hamadar Sahara.

Da suke jawabi yayin wani babban taro kan inganta samar da magunguna a yankin kudu da hamadar Sahara, da kamfanin hada magunguna na Takeda ya shirya, ayarin kwararrun sun bayyana cewa, galibin marasa lafiya ba sa zuwa asibiti sai cuta ta ci karfinsu, suna masu alakanta matsalar da rashin wayewar kai game da batutuwan da suka shafi lafiya ko kuma rashin cibiyoyin kiwon lafiya.

A nasa bangare, shugaban Kamfanin hada magunguna na Goodlife, Josh Ruxin, ya ce an sanya biliyoyin daloli domin yaki da cututtuka irinsu kanjamau da zazzabin cizon sauro da tarin fuka a yankin, inda ya ce an kuma samu kyakyawan sakamako.

Sai dai ya ce al'amarin ya sauya a yanzu, inda cututtuka musamman wadanda basa yaduwa, kamar ciwon zuciya da sukari da cutar daji ke haddasa mace-mace.

Ya ce akwai bukatar inganta tsarin kiwon lafiya tare da kara warewa bangaren kudade da nufin kara inganta ayyukan kula da lafiya da kuma magunguna ta yadda za su isa ga jama'a. ( Faiza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China