in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotun Masar ta ayyana kungiyar Hasm a matsayin kungiyar 'yan ta'adda
2017-02-12 12:52:39 cri
Jiya Asabar, kotun kula da harkokin gaggawa dake birnin Alkahira na kasar Masar ta yanke wani hukunci, inda ta ayyana kungiyar Hasm, wadda ke da alaka da kungiyar 'yan uwan musulmi a kasar, a matsayin kungiyar 'yan ta'adda. Wannan kungiya ta Hasm ta taba ikirarin daukar alhakin kai wasu jerin hare-hare a birnin Alkahira.

Bayan da sojojin Masar suka tsige Mohamed Morsi daga mukaminsa na shugaban kasa a watan Yulin shekara ta 2013, tsagerun masu tsattsauran ra'ayi sun kafa babban sansaninsu a zirin Sinai, da kaddamar da hare-hare da dama kan sojoji da 'yan sanda, lamarin da ya hallaka tare da raunata daruruwan mutane.

Shugaban hukumar leken asirin soja na kasar Masar Mohamed Faraj, ya bayyana a ranar Juma'ar data gabata cewa, tun da lokacin sojojin kasar suka kaddamar da gagaruman ayyukan murkushe 'yan ta'adda a watan Satumbar shekara ta 2015, zuwa yanzu, sojojin sun yi nasarar hallaka 'yan ta'adda kimanin 500 a zirin Sinai.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China