in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da fashewar bom a birnin Alkahira na kasar Masar a matsayin harin ta'addanci
2016-12-13 10:21:17 cri
Shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi, ya sanar a jiya Litinin cewa fashewar bom da ta auku a wani coci dake birnin Alkahira a ranar 11 ga wata harin ta'addanci ne na masu kunar bakin wake, kana an riga an tabbatar da wadanda suka kaddamar da harin na ta'addanci.

Shugaba al-Sisi ya bayyana cewa, matashin da ya kai harin ta'addancin dan kunar bakin wake ne mai suna Mahmoud Shafiq, kana an riga an kama saura mutane hudu da aka zarga da hannu cikin kitsa harin, kuma tuni hukumar kiyaye tsaro ta kasar ta fara neman wasu sauran mutane biyu dake da alaka da harin.

Da safiyar ranar Lahadi ne dai wani bam ya tashi a wata coci dake birnin Alkahira. Kana hukumar kiwon lafiya ta kasar ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu mutane 24 ne suka rasa rayukan su sakamakon fashewar, yayin da wasu mutanen 49 suka jikkata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China