Sanarwar ta bayyana cewa, wani mutum mai suna Abu Abdullah al-Masry ne ya kai harin kunar bakin wake.
A safiyar ranar Lahadi 11 ga wannan watan ne, a kai harin bom a wani coci dake yankin Abassiya na birnin Alkahira na kasar Masar.
Bisa kididdigar da aka yi, harin ya haddasa mutuwar mutane 24, yayin da mutane 49 suka ji rauni. (Zainab)